Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 11

Yahaya 11:5-16

Help us?
Click on verse(s) to share them!
5Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru.
6Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke.
7Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, “Bari mu je Yahudiya kuma.”
8Sai almajiransa suka ce masa, “Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?”
9Yesu ya amsa, “Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.
10Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi.
11Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, “Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci”.
12Sai almajirai suka ce masa, “Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka.”
13Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu.
14Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, “Li'azaru ya mutu.
15Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa.”
16Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, “Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu.”

Read Yahaya 11Yahaya 11
Compare Yahaya 11:5-16Yahaya 11:5-16