Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 1

Luka 1:40-54

Help us?
Click on verse(s) to share them!
40Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai

Read Luka 1Luka 1
Compare Luka 1:40-54Luka 1:40-54