Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 18

Luka 18:25-35

Help us?
Click on verse(s) to share them!
25Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
27Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
28Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
29Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
30sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.”
31Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
32Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
33Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
34Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
35Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,

Read Luka 18Luka 18
Compare Luka 18:25-35Luka 18:25-35