Text copied!
Bibles in Hausa

Luka 18:25-35 in Hausa

Help us?

Luka 18:25-35 in Litafi Mai-tsarki

25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.”
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
Luka 18 in Litafi Mai-tsarki