Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 1

Luka 1:33-48

Help us?
Click on verse(s) to share them!
33Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.”
34Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.

Read Luka 1Luka 1
Compare Luka 1:33-48Luka 1:33-48