Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 17

Luka 17:1-5

Help us?
Click on verse(s) to share them!
1Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'

Read Luka 17Luka 17
Compare Luka 17:1-5Luka 17:1-5