Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 23

Luka 23:13-22

Help us?
Click on verse(s) to share them!
13Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
14sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
15Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
16saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
17Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.
18Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
19Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
20Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
21Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
22Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”

Read Luka 23Luka 23
Compare Luka 23:13-22Luka 23:13-22