Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 1

Luka 1:54-65

Help us?
Click on verse(s) to share them!
54Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.”
56Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.

Read Luka 1Luka 1
Compare Luka 1:54-65Luka 1:54-65