Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Markus - Markus 8

Markus 8:24-32

Help us?
Click on verse(s) to share them!
24Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
25Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
26Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
27Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
28Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
29Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
30Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
31Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
32Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.

Read Markus 8Markus 8
Compare Markus 8:24-32Markus 8:24-32