Text copied!
Bibles in Hausa

Markus 8:24-32 in Hausa

Help us?

Markus 8:24-32 in Litafi Mai-tsarki

24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
Markus 8 in Litafi Mai-tsarki