Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 20

Luka 20:19-24

Help us?
Click on verse(s) to share them!
19Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
20Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
22Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24“Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”

Read Luka 20Luka 20
Compare Luka 20:19-24Luka 20:19-24