Text copied!
Bibles in Hausa

Luka 20:19-24 in Hausa

Help us?

Luka 20:19-24 in Litafi Mai-tsarki

19 Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
20 Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21 Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
22 Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24 “Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
Luka 20 in Litafi Mai-tsarki