22Mutanen suka yi ihu, “Wannan muryar allahce, ba ta mutum ba!”
23Nan take mala'ika Ubangiji ya buge shi don bai ba Allah daukaka ba, nan take tsutsotsi suka cinye shi har ya mutu.
24Maganar Allah ta yadu tana ta ribabbanya.
25Bayan Barnaba da Shawulu sun gama aikin su a Urushalima. Suna dawowa, suka zo tare da Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus ne. Barnaba da Shawulu suka koma Urushalima.