Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Markus - Markus 8

Markus 8:22-26

Help us?
Click on verse(s) to share them!
22Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
23Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
24Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
25Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
26Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”

Read Markus 8Markus 8
Compare Markus 8:22-26Markus 8:22-26