Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 9

Luka 9:20-24

Help us?
Click on verse(s) to share them!
20Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
21Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
22Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
23Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
24Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.

Read Luka 9Luka 9
Compare Luka 9:20-24Luka 9:20-24