Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 6

Luka 6:22-29

Help us?
Click on verse(s) to share them!
22Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
23Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
24Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
25Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
26Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
27Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
28Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
29Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.

Read Luka 6Luka 6
Compare Luka 6:22-29Luka 6:22-29