20Allah na salama zai sa ku tattake Shaidan da sauri kalkashin sawayen ku. Alherin Ubangijin mu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku.
21Timoti abokin aikina, yana gaishe ku, haka Lukiyas da Yason da Susibataras da kuma yan'uwana.
22Ni Tartiyas wanda ya rubuta wasikan nan, na gaisheku cikin Ubangiji.
23Gayus mai masaukina da kuma dukan Ikilisiya, suna gaishe ku. Arastas ma'ajin birni na gaishe ku, da Kwartus dan'uwanmu.
24Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku dukka. Amin.