Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 17

Luka 17:4-8

Help us?
Click on verse(s) to share them!
4Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?

Read Luka 17Luka 17
Compare Luka 17:4-8Luka 17:4-8