Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Markus - Markus 9

Markus 9:28-36

Help us?
Click on verse(s) to share them!
28Da Yesu ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi a kadaice, me ya sa muka kasa fitar da shi?”
29Ya ce masu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a.”
30Sai suka ratsa cikin Galili, amma ba ya son kowa ya san inda suke.
31Da yake koyar da almajiransa, ya ce masu lokaci na zuwa da za'a ba da Dan mutum a hannun mutane, za su kuwa kashe shi, sa'adda aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.
32Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa.
33Sai suka zo kafarnahum. A lokacin da ya ke cikin gida, ya tambayi Al'majiransa, Menene ku ke magana a kansa a hanya?
34Amma suka yi shiru. don suna gardama da junansu akan hanya, a kan wane ne mafi girma.
35Sai ya zauna, ya kira al'majiransa goma sha biyu, yace masu duk wanda ya ke so ya zama na fari, dole ya kankantar da kansa, sa'annan ya bautawa sauran duka.
36Sai ya dauko karamin yaro a hannunsa ya sa shi a tsakiyarsu. Ya rumgome shi a kafadarsa ya ce masu.

Read Markus 9Markus 9
Compare Markus 9:28-36Markus 9:28-36