Text copied!
Bibles in Hausa

Markus 9:28-36 in Hausa

Help us?

Markus 9:28-36 in Litafi Mai-tsarki

28 Da Yesu ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi a kadaice, me ya sa muka kasa fitar da shi?”
29 Ya ce masu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a.”
30 Sai suka ratsa cikin Galili, amma ba ya son kowa ya san inda suke.
31 Da yake koyar da almajiransa, ya ce masu lokaci na zuwa da za'a ba da Dan mutum a hannun mutane, za su kuwa kashe shi, sa'adda aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.
32 Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa.
33 Sai suka zo kafarnahum. A lokacin da ya ke cikin gida, ya tambayi Al'majiransa, Menene ku ke magana a kansa a hanya?
34 Amma suka yi shiru. don suna gardama da junansu akan hanya, a kan wane ne mafi girma.
35 Sai ya zauna, ya kira al'majiransa goma sha biyu, yace masu duk wanda ya ke so ya zama na fari, dole ya kankantar da kansa, sa'annan ya bautawa sauran duka.
36 Sai ya dauko karamin yaro a hannunsa ya sa shi a tsakiyarsu. Ya rumgome shi a kafadarsa ya ce masu.
Markus 9 in Litafi Mai-tsarki