Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 23

Luka 23:5-12

Help us?
Click on verse(s) to share them!
5Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
6Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
7Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
8Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
9Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
10Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
11Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
12Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).

Read Luka 23Luka 23
Compare Luka 23:5-12Luka 23:5-12