Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 1

Luka 1:45-50

Help us?
Click on verse(s) to share them!
45Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.

Read Luka 1Luka 1
Compare Luka 1:45-50Luka 1:45-50