Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Romawa - Romawa 10

Romawa 10:10-17

Help us?
Click on verse(s) to share them!
10Don da zuciya ne mutum yake gaskatawa zuwa ga adalci, da kuma baki ne yake shaida zuwa ga ceto.
11Don nassi na cewa, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai ji kunya ba,”
12Gama ba bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'ume. Gama dukkansu Ubangijinsu daya ne, Shi mayalwaci ne ga dukkan wanda ya kira shi.
13Duk wanda ya kira sunan Ubangiji zai sami ceto.
14To ta yaya zasu kira ga wanda basu gaskata ba? Kuma ta yaya zasu gaskata ga wanda ba su taba jin labarinsa ba?
15Kuma ta yaya zasu ji in ba ayi masu wa'azi ba? Kuma ta yaya zasu yi wa'azin in ba an aike su ba? - Kamar yadda yake a rubuce, “Ina misalin kyau na kafafun wadanda ke shaida labarin farin ciki na abubuwa masu kyau!”
16Amma ba dukkansu ne suka ji bishara ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata da sakon?
17Saboda haka bangaskiya na zuwa ta wurin ji, jin kuwa daga maganar Almasihu.

Read Romawa 10Romawa 10
Compare Romawa 10:10-17Romawa 10:10-17