Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 4

Luka 4:29-37

Help us?
Click on verse(s) to share them!
29Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
30Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
31Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
32Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
33A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
34“Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
35Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
36Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
37Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.

Read Luka 4Luka 4
Compare Luka 4:29-37Luka 4:29-37