40Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
41Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
42Sai suka bashi gasasshen kifi.
43Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
44Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
45Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
46Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.