14Saminu ya fada yadda Allah ya fara nuna jinkai ga al'ummai domin ya dauke jama'a daga cikinsu domin sunansa.
15Maganar annabawa ta yarda da wannan, kamar yadda yake a rubuce,
16'Bayan wadannan abubuwa zan dawo, zan gina gidan Dauda wanda ya fadi kasa; in sake gina bangonsa, in tsayar da shi,
17saboda sauran jama'a su nemi fuskar Ubangiji, har da al'ummai da ake kira da sunana.