34Yesu ya ce masu, “Hakika, hakika, ina ce maku, dukan wanda ya ke aika zunubi bawan zunubi ne.
35Bawa kuwa, ba ya zama a gida dindindin, da yana zama dindindin.
36Saboda haka, idan Dan ya 'yantar da ku zaku zama 'yantattu sosai.
37Na san ku zuriyar Ibrahim ne, kuna so ku kashe ni saboda kalma ta bata da wurin zama a cikin ku.
38Na fadi abubuwan da na gani a wurin Ubana, ku kuma kuna yin abubuwan da kuka ji daga wurin ubanku.”