Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 7

Yahaya 7:23-30

Help us?
Click on verse(s) to share them!
23Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
24Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
25Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
26Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
27da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
28Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
29Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
30Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.

Read Yahaya 7Yahaya 7
Compare Yahaya 7:23-30Yahaya 7:23-30