4(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
5Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
6(Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”