14Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.
15Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu.
16Suka ce, “Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka.