Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 9:6-14 in Hausa

Help us?

Yahaya 9:6-14 in Litafi Mai-tsarki

6 Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
Yahaya 9 in Litafi Mai-tsarki