Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 9

Yahaya 9:6-14

Help us?
Click on verse(s) to share them!
6Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.

Read Yahaya 9Yahaya 9
Compare Yahaya 9:6-14Yahaya 9:6-14