Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 5:38-46 in Hausa

Help us?

Yahaya 5:38-46 in Litafi Mai-tsarki

38 Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39 Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata.
40 kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.
41 Ba na karbar yabo daga wurin mutane,
42 amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi.
44 Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?
45 Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa.
46 Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni.
Yahaya 5 in Litafi Mai-tsarki