Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 5

Yahaya 5:38-46

Help us?
Click on verse(s) to share them!
38Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata.
40kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.
41Ba na karbar yabo daga wurin mutane,
42amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.
43Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi.
44Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?
45Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa.
46Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni.

Read Yahaya 5Yahaya 5
Compare Yahaya 5:38-46Yahaya 5:38-46