Text copied!
Bibles in Hausa

Romawa 3:16-24 in Hausa

Help us?

Romawa 3:16-24 in Litafi Mai-tsarki

16 Tafarkinsu wahala ce da lalacewa.
17 Wadannan mutane basu san hanyar salama ba.
18 Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah.
20 Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
21 Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa.
22 Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
23 Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah,
24 Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
Romawa 3 in Litafi Mai-tsarki