Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 2

Luka 2:22-36

Help us?
Click on verse(s) to share them!
22Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
23Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
24Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
25Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
26An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
28sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
29“Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30Domin idanuna sun ga cetonka,
31wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
32Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
33Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
34Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
35Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
36Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,

Read Luka 2Luka 2
Compare Luka 2:22-36Luka 2:22-36