22 Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24 “Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
25 Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”