Text copied!
Bibles in Hausa

Luka 1:49-72 in Hausa

Help us?

Luka 1:49-72 in Litafi Mai-tsarki

49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.”
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai.
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Luka 1 in Litafi Mai-tsarki