Text copied!
Bibles in Hausa

Luka 18:37-43 in Hausa

Help us?

Luka 18:37-43 in Litafi Mai-tsarki

37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
Luka 18 in Litafi Mai-tsarki