13 Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14 Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa.
15 Ina sa bege ga Allah, kamar yadda za a yi tashin matattu, masu adalci da miyagu;
16 a kan haka kuma, nake kokarin zama mara abin zargi a gaban Allah da mutane ina yin haka cikin dukan al'amura.
17 Bayan wadansu shekaru na zo in kawo wasu sadakoki da baikon yardar rai.
18 Cikin kudurin yin haka, sai wasu Yahudawa daga kasar Asiya suka iske ni a cikin ka'idodin tsarkakewa a haikali, ba da taro ko ta da hargitsi ba.
19 Yakamata wadannan mutanen su zo gabarka a yau, har idan suna da wani zargi a kai na.
20 In kuwa ba haka ba bari mutanennan su fada in sun taba iske ni da wani aibu a duk lokacin da na gurfana a gaban majalisar Yahudawa;