12Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba.
13Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa.