12 Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba.
13 Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14 Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa.