Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 9:32-39 in Hausa

Help us?

Yahaya 9:32-39 in Litafi Mai-tsarki

32 Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba.
33 In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
Yahaya 9 in Litafi Mai-tsarki