Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 9:26-35 in Hausa

Help us?

Yahaya 9:26-35 in Litafi Mai-tsarki

26 Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba.
33 In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
Yahaya 9 in Litafi Mai-tsarki