Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 7:40-51 in Hausa

Help us?

Yahaya 7:40-51 in Litafi Mai-tsarki

40 Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
41 Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne.?
42 Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
43 Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
44 Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45 Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
46 Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
47 Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
48 Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
49 Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
50 Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
51 “Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
Yahaya 7 in Litafi Mai-tsarki