Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 7:16-20 in Hausa

Help us?

Yahaya 7:16-20 in Litafi Mai-tsarki

16 Yesu ya ba su amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
17 Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
18 Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19 Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
20 Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
Yahaya 7 in Litafi Mai-tsarki