47 Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami.
48 Ni ne Gurasa ta rai.
49 Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50 Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
51 Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.”