Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 6:30-35 in Hausa

Help us?

Yahaya 6:30-35 in Litafi Mai-tsarki

30 Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
35 Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
Yahaya 6 in Litafi Mai-tsarki