Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 6:29-34 in Hausa

Help us?

Yahaya 6:29-34 in Litafi Mai-tsarki

29 Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
30 Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
Yahaya 6 in Litafi Mai-tsarki