Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 5:19-22 in Hausa

Help us?

Yahaya 5:19-22 in Litafi Mai-tsarki

19 Yesu ya amsa masu ya ce, hakika hakika, ina gaya maku, Dan ba ya yin kome shi kadai, sai abin da ya ga Uba yana yi.
20 Domin Uban na kaunar Dan, yana kuma nuna masa dukan abinda shi da kansa yake yi, kuma zai nuna masa abubuwan da suka fi wadannan, domin ku yi mamaki.
21 Gama kamar yadda Uba yakan tada matattu ya kuma basu rai, haka Dan ma yake bada rai ga duk wanda ya nufa.
22 Gama Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya damka dukan hukunci ga Dan,
Yahaya 5 in Litafi Mai-tsarki